1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Nijar ya ce zai kare dimukuradiyya

July 28, 2023

Bayan kwace gwamnati da sojoji suak yi a Nijar, shugaban kasar ya yi alkawarin kare nasarorin dimukuradiyyar kasar da aka samu ta hanyar gagarumar gwagwarmaya.

Mohamed Bazoum
Hoto: Ludovic Marin/AFP

Kwana guda bayan sanar da kwace gwamnati, hambarerren Shugaba Mohamed Bazoum na Jamhuriyar Nijar ya sha alwashin kare nasarorin dimukuradiyyar da ya ce an same su da tsayin daka.

A daren ranar Larabar da ta gabata ce dai sojoji a Nijar din suka ayyana kwace iko daga Bazoum, suka kuma rusa kundin mulki tare da dakatar da duk wani tsari na farar hula a kasar.

Mohamed Bazoum wanda ba a kaiga sanin inda yake ba tun bayan aukuwar lamarin, ya yi alkawarin cewa 'yan Nijar masoya dimukuradiyya ne ke da nasara a karshen wannan lamari.

Kasar Amurka da ma Majalisar Dinkin Duniya, duk sun yi alkawarin bai wa Bazoum cikakken goyon baya a halin da yake ciki.

Wannan ne juyin mulki karo na bakwai da ake gani a yankin yammaci da ma tsakiyar Afirka, daga shekara ta 2020 zuwa yanzu.