Shugaban palasdinawa ya nemi taimakon komitin sulhu akan izraela
November 4, 2006Talla
Shugaba Mahmoud Abbas na yankin Palasdinawa yayi kira ga komitin sulhun mdd ,daya taimaka wajen dakatar da hare haren da dakarun Israela ke cigaba dayi a zirin Gaza.A jiya nedai sakatare general na mdd Kofi Annan yayi kira ga Izraelan data nuna halin sanin yakamata ,adangane da sabbin somame data fara yi a yankin palasdinawan wanda a jiya jumaa kadai,ya kashe palasdinawa 19.A jiyan dai mata biyu ne suka rasa rayukansu a wannan yankin,kisan da Amurka tayi nadama dashi,duk dacewa ta danganta harin izraelan da martani kann harin rokoki da palasinawan suka kai musu.