SiyasaArewacin Amurka
Shugabannin BRICS sun bukaci kawo karshen yakin Gaza
July 6, 2025
Talla
Shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya jaddada kira ga kasashen duniya wajen kawo karshen abin da ya kira karshen "kare dangi" da Isra'ila ke yi a Gaza, a daidai lokacin da shugabannin kasashe 11 masu karfin tattalin arziki na BRICS ke kammala taronsu a birnin Rio de Janeiro.
Karin bayani: BRICS na tsara tunkarar manufofin shugaban Amurka Trump
An dai samu rarrabuwar kawuna dangane da yadda kasashen na BRICS ke nazari kan yakin Gaza da kuma bayyana ra'ayinsu kan gumurzun kwanaki 12 da Isra'ila ta yi da Iran. Kalaman Shugaban Brazil na zuwa a daidai lokacin ake sa ran Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu zai gana da Donald Trump a gobe Litinin 8 ga watan Yuli, a can fadar White House na Amurka.