1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin duniya sun soki harin Faransa

Abdullahi Tanko Bala
October 29, 2020

Shugabannin kasashen duniya sun yi Allah wadai da harin da aka kai da wuka a birnin Nice na kasar Faransa wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane uku. Masu bincike a Faransa na daukar harin a matsayin na ta'addanci.

Frankreich Nizza | Messerattacke | Präsident Emmanuel Macron
Hoto: Gaillard Eric/abaca/picture alliance

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce ta kadu matuka da harin ta kuma jajantawa iyalan wadanda suka rasu. A nata bangaren shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula von der Layen itama ta yi Allah wadai da harin wanda ta ce babu imani a cikinsa.

Firaministan Italiya Giuseppe Conte yace harin ba zai kassara kudirinsu na kare yancin fadin albarkacin baki da wanzar da zaman lafiya ba. Shima da yake tsokaci Firaministan Spain Pedro Sanchez yace tarayyar turai kan su a hade yake wajen adawa da nuna kiyayya kuma za su cigaba da kare yanci da akidun dimukuradiyya da kuma tsaron yan kasa.

Firaministan Birtaniya Boris Johnson a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter yace mummunan labarin harin da aka kai a mujami'ar Notre-Dame ya girgiza shi matuka. Shugabannin Turan na gudanar da taro ta kafar bidiyo domin nazarin halin da ake ciki.