1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya: Gwamnati ta kwaci Deir Ezzor daga IS

Salissou Boukari
November 3, 2017

Sojojin gwamnatin Siriya masu samun goyon bayan Rasha sun kwace birnin Deir Ezzor daga hannun mayakan IS a cewar kungiyar da ke sa ido kan kare hakin bil-Adama ta (OSDH) a kasar ta Siriya.

Syrien Krieg - Kämpfe in Deir ez-Zor
Hoto: Getty Images/AFP

Tun dai a jiya kafofin yada labaran gwamnatin ta Siriya suka sanar cewa akwai babban ci gaba da dakarun gwamnatin ke samu a birnin na Deir Ezzor yanki mai arzikin man fetur da ke gabashin kasar iyaka da Iraki. Sai dai kuma a hakumance gwamnatin ta Siriya ba ta ayyana kwace birnin ba. Hakan dai na kara tabbatar da irin mawuyacin halin da 'yan kungiyar ta IS ke ciki a halin yanzu, inda take ci gaba da fuskantar babban koma baya. 

Kungiyar kare hakin bil-Adama ta kasar ta Siriya mai cibiya a birnin London na Britaniya ta OSDH, ta ce an dakatar da harbe-habe, kuma tuni aka soma ayyukan tone nakiyoyi da 'yan jihadin suka bizne a wurare daban-daban. Sai dai kuma wata majiya ta sojan kasar ta Siriya ta ce sun dai kwace sama da kashi 80 ne na birnin.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW