Siyasa gabannin rantsar da Tinubu
May 11, 2023![](https://static.dw.com/image/62069042_800.webp)
Talla
Jam'iyyu biyar da ke kalubalantar nasarar da Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa a watan Fabirairun da ya gabata sun fara bayyana dalilansu a gaban kotun sauraren kararrakin zaben zaben shugaban kasa da gwamnoni da 'yan majalisun tarayya. Wannan na zuwa ne makonni kalilan kafin rantsar da zababbun a karshen watan Mayu.