1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Siyasar Senegal: An bude rumfunan zaben shugaban kasa

March 24, 2024

Dubban jama'a ne suke fito domin sauke nauyin da ke wuyansu na zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokoki a Senegal, bayan dambarwar siyasar da ta mamaye kasar harma da batun rashin tabbas kan makomar siyasar kasar.

Wata mata a lokacin kada kuri'a a zaben 'yan majalisar wakilai na 2022 a Senegal.
Wata mata a lokacin kada kuri'a a zaben 'yan majalisar wakilai na 2022 a Senegal.Hoto: Johan Wessels/AFP

Kimanin Mutane  milyan 7.3 ne sukayi rajistar kada kuri'a a kasar ta Senegal da ke yammacin Afrika. A dokar kasar za a rufe rumfunan zabe da misalin karfe 6 na yamma agogon GMT, inda za a sanar da sakamakon zaben a cikin mako mai zuwa.

Karin bayani: 'Yan takarar shugaban kasa a Senegal sun kaddamar da yakin zabe

Daruruwan masu sa ido ne suka isa Senegal, kasar da ke rike da kambun gudanar da sahihin zabe da kuma bunkasar dimukradiyya a yankin kasashen yammacin Afrika. Rahotannin sun tabbatar da isar masu sa ido daga kungiyoyin fararen hula da kungiyar raya kasashen Afrika ta AU da kungiyar bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS harma da wakilcin kungiyar tarayyar Turai EU.

Karin bayani:Diomaye Faye ya samu goyon bayan Karim Wade a zaben Senegal 

Dukkan 'yan takarar da suke shiga zaben sun yi hasashen samun nasara a zagayen farko kama daga dan takarar da ke samun goyon bayan shugaban kasar mai barin gado Macky Sall wato Amadou Ba da 'dan takarar da ke samun goyon bayan Karim Wade da aka haramta masa takara wato Bassirou Diomaye Faye harma da tsohon magajin garin birnin Dakar Khalifa Sall.