1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojan da ke yakar IS sun bude wuta a Raqa

Yusuf Bala Nayaya
February 4, 2017

Babban burin fadan dai na zama na ganin an kwace kafatanin yankin da IS ke iya tasiri a birnin Raqa da ke Siriya da tuni ake fafatawa da mayakan na IS tun a shekarar bara.

Syrien SDF PK Sturm auf Rakka
Hoto: Getty Images/AFP/D. Souleiman

Dakarun Kurdawa da Larabawa da ke samun goyon bayan Amirka a Arewacin Siriya sun bayyana a ranar Asabar din nan cewa sun kaddamar da sabbin hare-hare kan mayakan IS a wasu garuruwa da kauyuka da ke Arewacin birnin Raqa. Sojan gwagwarmayar kare dimukaradiyya sun bayyana a ranar Asabar din nan cewa sun koma filin daga, a ta bakin Cihan Sheikh Ehmed da ke magana da yawun dakarun , ta ce sun shiga kaso na uku na fafutikar kwace Raqa fadan da aka fara tun a watan Nuwambar bara.

Babban burin fadan dai na zama na ganin an kwace kafatanin yankin da IS ke iya tasiri a birnin. Wannan jawabi dai na zuwa ne kwana guda bayan da jirgin sama bisa jagorancin Amirka ya yi raga-raga da wata gada a wannan yanki da kungiyar ta IS ke taka rawar gaban hantsi.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW