1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Soji hudu sun rasa ransu a Mali

April 2, 2021

Masu ikirarin jihadi a Mali sun yi yunkurin kutsawa sansanin dakarun Majalisar Dinkin Duniya, inda suka fafata da sojojin kawance, lamarin da ya salwantar da rayukan dakarun MINISMA.

Mali Vereinte Nationen MINUSMA Mission
Hoto: picture-alliance/dpa/Le Pictorium/N. Remene

Wani harin da ake zargin masu ikirarin jihadi da kaddamar da shi ya halaka dakarun da ke aikin  wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Mali. Rundunar MINUSMA ita ce ta tabbatar da kisan dakarun na Majalisar Dinkin Duniya hudu yayin da wasu sojoji da dama suka jikkata. Harin dai ya afku ne a wani wuri mai nisan kilomitoci 200 da kan iyakar kasar ta Mali da Aljeriya.

Dakarun sun ce mayakan dauke da muggan makamai sun yi yunkurin kutsa kai a sansanin sojin da ke Aguelhok na arewacin Mali inda suka hana su shiga tare kuma da halaka 'yan ta'addan guda biyar.