1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Soji hudu sun rasa ransu a Mali

April 2, 2021

Masu ikirarin jihadi a Mali sun yi yunkurin kutsawa sansanin dakarun Majalisar Dinkin Duniya, inda suka fafata da sojojin kawance, lamarin da ya salwantar da rayukan dakarun MINISMA.

Mali Vereinte Nationen MINUSMA Mission
Hoto: picture-alliance/dpa/Le Pictorium/N. Remene

Wani harin da ake zargin masu ikirarin jihadi da kaddamar da shi ya halaka dakarun da ke aikin  wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a Mali. Rundunar MINUSMA ita ce ta tabbatar da kisan dakarun na Majalisar Dinkin Duniya hudu yayin da wasu sojoji da dama suka jikkata. Harin dai ya afku ne a wani wuri mai nisan kilomitoci 200 da kan iyakar kasar ta Mali da Aljeriya.

Dakarun sun ce mayakan dauke da muggan makamai sun yi yunkurin kutsa kai a sansanin sojin da ke Aguelhok na arewacin Mali inda suka hana su shiga tare kuma da halaka 'yan ta'addan guda biyar.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW