1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Amirka za su bar Nijar a watan Satumbar 2024

May 19, 2024

Amirka ta ce za ta fara janye dakarunta daga Jamhuriyar Nijar, inda ake sa ran a kammala kwashe su zuwa ranar 15 ga watan Satumbar 2024.

Amirka za ta kammala kwashe sojojinta daga Nijar a Satumbar 2024
Amirka za ta kammala kwashe sojojinta daga Nijar a Satumbar 2024Hoto: Alex Fox Echols Iii/Planetpix/ZUMAPRESS.com/picture alliance

A cikin sanarwar hadin gwiwa da Amirka da kuma majalisar mulkin sojin Nijar suka fitar, sun ce sun cimma matsayar ne kan fara kwashe dakarun bisa bukatar gwamnatin sojin sakamakon zargin da ta yi na girke su ba bisa ka'ida ba.

Karin bayani: Amirka na shirin janye dakarunta daga Nijar

Kazalika bangarorin sun cimma yarjejeniyar bayar da kariya ga sojojin Amirka har zuwa lokacin da za a kammala janye su. Wannan matakin dai na zuwa ne bayan da tawagar Amirka da sojojin Nijar suka kwashe kwanaki suna tattauna wa kan jadawalin aikin kwashe dakarun.

Karin bayani: Amirka na son ci gaba da yin hulda da Nijar

Tun bayan da sojoji suka kwace mulkin Nijar a shekarar 2023, majalisar sojin kasar ta soke yarjejeniyar tsaro tsakaninta da gwamnatin Washington tare da katse alakarta da uwargijiyarta Faransa, yayin da a gefe guda ta karfafa alaka da kasar Rasha.