1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Burkina Faso: An kashe gwamman 'yan ta'adda

Abdoulaye Mamane Amadou LMJ
November 9, 2021

A Burkina Faso wani artabu da sojinin kasar suka yi da 'yan ta'adda ya yi sanadiyyar mutuwar mayakan jihadi 15 a lardin Komadjari a yayin dakile wani mummunan harin da suka kudiri anniyar kaiwa.

Burkina Faso Symbolbild Anschlag
Hoto: Sia Kambou/AFP

Ma'aikatar tsaron kasar Burkina Faso ta ce wani sojanta daya ya rasu a yayin batakashin tare da kuma raunata wasu uku. Sai dai ko ba'idinsa rundunar tsaron ta Burkina Faso ta ce ta yi nasarar kwace muggan makamai a hannun mayakan ciki har da baburan da suke kai wa dakarun tsaron kasar hari da su.

Tun a shekarar 2015 ne dai kasar mai makwaftaka da Mali da Jamhuriyar Nijar ke fuskantar hare-haren 'yan bindiga masu tsananin kishin addini, inda rahotanni suka ce an halaka fiye da mutum dubu biyu, wasu fiye da miliyan daya suka kauracewa gidajensu don tsira da ransu.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW