Sojin Najeriya sun kashe yan Boko Haram 50
October 23, 2025
Talla
Najeriya kasa mafi yawan jama'a a Afirka ta dade tana fama da 'yan kungiyar Boko Haram da na ISWAP a yammacin Afirka kusan shekaru 16 a kokarin da mayakan jihadin ke yi na kafa daula arewa maso gabashin kasar.
Da sanyin safiyar alhamis ne sojojin Najeriyar tare da rakiyar jiragen yaki suka far ma 'yan tada kayar bayan da suka kai hare hare a garuruwan Dikwa da Mafa da Gajibo a jihar Borno da kuma Katarko a jihar Yobe mai makwabtaka a cewar Leftanar kanar Sani Uba mai magana da yawun sojojin kamar yadda ya fada a cikin wata sanarwa.
Sai dai kuma sojojin basu fadi kungiyar da ta kai hare haren ba amma bayanan sirri na cewa 'yan kungiyar ISWAP ne suka kai harin.