SiyasaAfirka
Sojojin Sudan sun fara sako fararen hula
November 22, 2021
Talla
Shugaban jam'iyyar Congress Party Omar al-Degeir ya ce tun a yammacin Lahadi sojojin suka sako shi ya koma gidansa. Sauran wadanda aka sako din sun hada da 'yan siyasar jam'iyyar Umma Party da sauran wasu jami'ai.
Kasashen duniya sun yi maraba da mayar wa da Firaminista Hamdok mulkinsa bayan hambarar da shi da aka yi. Sai dai kuma Ministar Kula da Harkokin Kasashen Afirka ta Burtaniya Vicky Ford ta gargadi sojojin da lallai su martaba yarjejeniyar da aka kulla da su gabanin mika mulkin ga Hamdok.