1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Sojojin Isra'ila za su dakatar da fada a wurare uku a Gaza

July 27, 2025

Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila ne a kan halin jin kai da Gaza ke ciki.

Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila a kan halin jinkai da Gaza ke ciki.
Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila a kan halin jinkai da Gaza ke ciki.Hoto: Jack Guez/AFP/Getty Images

Sojojin Isra'ila sun fada a ranar Lahadi cewa za su dakatar da fada a yankuna uku na zirin Gaza a matsayin wani mataki na rage tsananin halin jin kai da ake ciki.

Sojojin sun ce za su dakatar da ayyuka a Muwasi da Deir al-Balah da kuma cikin birnin Gaza daga karfe 10:00 na safe zuwa 8:00 na dare agogon yankin a kowace rana har sai an bayar da wani sabon umarni.

Faransa za ta amince da Kasar Falasdinu

A cikin wata sanarwa, sojojin sun ce za su bayyana hanyoyin da za a bi domin taimaka wa kungiyoyin agaji wajen isar da abinci da sauran kayan tallafi ga jama'a a fadin Gaza.

Sojojin sun kuma ce ba sa fada a wadannan yankuna, amma an samu tashin hamkali da hare-hare a dukkansu a cikin 'yan makonnin nan da suka gabata.

'Yan majalisun dokokin Burtaniya 221 sun bukaci amincewa da kasar Falasdinu

A baya-bayan nan kasashen duniya sun rika sukar Isra'ila da ta bari a shigar da kayan agaji da abinci zirin Gaza saboda yadda yunwa ke kassara mutane ciki har da mata da yara kanana.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW