1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Sojojin Isra'ila za su dakatar da fada a wurare uku a Gaza

July 27, 2025

Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila ne a kan halin jin kai da Gaza ke ciki.

Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila a kan halin jinkai da Gaza ke ciki.
Sanarwar ta biyo bayan matsin lamba da aka rika yi wa Isra'ila a kan halin jinkai da Gaza ke ciki.Hoto: Jack Guez/AFP/Getty Images

Sojojin Isra'ila sun fada a ranar Lahadi cewa za su dakatar da fada a yankuna uku na zirin Gaza a matsayin wani mataki na rage tsananin halin jin kai da ake ciki.

Sojojin sun ce za su dakatar da ayyuka a Muwasi da Deir al-Balah da kuma cikin birnin Gaza daga karfe 10:00 na safe zuwa 8:00 na dare agogon yankin a kowace rana har sai an bayar da wani sabon umarni.

Faransa za ta amince da Kasar Falasdinu

A cikin wata sanarwa, sojojin sun ce za su bayyana hanyoyin da za a bi domin taimaka wa kungiyoyin agaji wajen isar da abinci da sauran kayan tallafi ga jama'a a fadin Gaza.

Sojojin sun kuma ce ba sa fada a wadannan yankuna, amma an samu tashin hamkali da hare-hare a dukkansu a cikin 'yan makonnin nan da suka gabata.

'Yan majalisun dokokin Burtaniya 221 sun bukaci amincewa da kasar Falasdinu

A baya-bayan nan kasashen duniya sun rika sukar Isra'ila da ta bari a shigar da kayan agaji da abinci zirin Gaza saboda yadda yunwa ke kassara mutane ciki har da mata da yara kanana.