Sojojin Kamaru sun kashe 'yan Boko Haram sama da 100
September 9, 2014Talla
A cewar mai magana da yawun gwamnatin ƙasar ta Kamaru Issa Tchiroma Bakary da ya ke jawabi ta kafar gidan rediyo na ƙasar. Ya ce dakarun sojin na Kamaru sun yi babbar illa ga Ƙungiyar ta Boko Haram a fafatawar da suka yi da su a ranar Asabar a yanki arewa mai nisa na Kamarun.
Yazuwa yanzu dai babu wata kafa da ta tabbatar da gaskiyya wannan labari, kuma hukumomin na Kamaru sun rufe ɗaukacin makarantun da ke a yankin na arewa mai nisa saboda dalilan tsaro.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu