1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hanyoyin neman kawo karshen rikicin siyasar Sudan

Suleiman Babayo MAB
April 30, 2019

Mahukuntan gwamnatin mulkin sojan Sudan sun ce suna shirye da ganin kawo karshen rikicin siyasar kasar ta hanyar tattauna mafita da 'yan adawa da kuma masu zanga-zanga.

Sudan | Protest | Militär in Khartoum
Hoto: Reuters/U. Bektas

Sojojin da ke rike da madafun iko a Sudan sun tabbatar da cewa suna shirye da ci gaba da tattaunawa da 'yan adawa domin tantance makomar kasar. Mataimakin shugaban gwamnatin mulkin ta wucen gadi Manjo-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya bayyana haka inda ya ce suna neman hanyar ganin kawo karshen zaman dirshen da masu zanga-zanga ke yi cikin tsanaki da kwanciyar hankali.

Masu zanga-zanga na neman ganin kafa gwamnati ta fararen hula domin tsara mika mulki tun bayan nasarar da masu zanga-zangar suka samu ta kawar da gwamnatin tsohon Shugaba Omar al-Bashir ranar 11 ga wannan wata na Afrilu, bayan da ya shafe kimanin shekaru 30 yana mulkin kama karya a kasar ta Sudan.