1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari a wani Otel ya yi sanadiyyar rayuka

Binta Aliyu Zurmi
October 23, 2022

Wani harin ta'addanci da mayakan Al-Shabaab suka kai a wani Otel da ke kudancin kasar Somaliya ya yi sanadiyar rayukan mutane 4 a cewar shaidun gani da ido.

Hoto: Str./AFP

Jami'an tsaro da suka tabbatar da harin, sun ce mota shake da ababen fashewa ta kutsa cikin Otel din Tawakal a garin Kismayo a wannan Lahadi.

Wannan harin dai bai zo da mamaki ba don ko baya ga jami'an gwamnati da mayakan na Al-Shabaab suka saba kai wa farmaki sukan yi hakan a kan fararen hula a cewar wani jami'in 'yan sanda Abdullahi Isma'ail.

Sama da shekaru 15 ke nan kungiyar Al-Shabaab ke kokarin kifar da gamnatin farar hula a kasar, inda ta ke kai harin kan mai uwa da wabi a kan jami'an tsaro da kuma al'umma.

A shekarar 2019 an kai wani hari makamancin wannan a wani Otel da ya salwantar da rayukan mutum sama da 20 tare da jikkata wasu mutum 117.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW