Somaliya za ta raba fararen hula da makamai
August 14, 2014![](https://static.dw.com/image/17842854_800.webp)
Talla
Gwamnatin Somaliya ta kaddamar da sabon shirin karbar makamai daga hannu mutane, tare da samun nasarar karbe makamai kimanin 5000. Lamarin ya haifar da musayar wuta a birnin Mogadishu fadar gwamnatin kasar. Jami'ai sun kaddamar da aikin kafin makamai su shiga hannu mayakan wadanda suke da dangantaka da al-Qaeda.
Dakarun sun caje gidan wani jami'an soji da aka samu makamai da ake zargin za a sayar wa 'yan al-Shabaab. Tuni aka kama jami'in. Kasuwar sayar da makamai ta yi kaurin suna a kasar ta Somaliya wadda shugabannin kabilu ke tafiyarwa tun cikin shekarun 1990.
Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mohammad Nasiru Awal