Steinmeier na iya zama shugaban Jamus
November 14, 2016![Frank-Walter Steinmeier ASEM Asien Europa Treffen Luxemburg](https://static.dw.com/image/18831182_800.webp)
A ranar Litinin din nan ce jam'iyyu da ke kawance da jam'iyyar shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel suka amince da zabin ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier don ya zama dan takarar shugabancin kasar a zaben da ke tafe shekara mai zuwa. Wannan dai na nufin sai an sake kwaskwarima a majalisar zartarwar kasar ta Jamus.
Kawancen Jam'iyyun da CSU sun amince da zabin na Steinmeier don kaucewa gwama numfashi da jam'iyyarsa ta SPD a kokarinsu na ganin damar ba ta kwace wa aminansu da ke cikin kawancen gwamnati ba.
Shugaban jam'iyyar ta SPD Sigmar Gabriel ya ce lokaci ya yi wuri a fara batun wanda zai maye gurbin Steinmeier a matsayin ministan harkokin kasashen waje. A watan Fabrariru ne dai za a yi zaben shugaban kasar wanda Steinmeier ke fatan zama shugaban na Jamus inda zai maye gurbin Shugaban kasar mai barin gado Joachim Gauck.