1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: al-Bashir ya soki masu bore

Abdul-raheem Hassan
January 27, 2019

Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya caccaki masu boren neman kawo karshen shugabancinsa da cewa suna kwaikwayon salon guguwar neman sauyi da ya mamaye kasashen Larabawa a yankin Gabas ta tsakiya a shekarun baya.

Suadan Präsident Omar Al Bashir
Hoto: Reuters/M. Abdallah

al-Bashir ya bayyana haka ne a yayin da yake ziyara a makwabciyar kasarsa wato Masar, inda ya zargi wasu kungiyoyin da ingiza wutar rikici kasashe kamar Sudan.

Hukumomi sun ce akalla mutane 30 ne suka mutu tun bayan fara zanga-zangar neman kawo karshen shugabancin sama da shekaru 30 na Shugaba al-Bashir. Amma wasu kungiyoyin kare fararen hula sun ce sama da mutane 45 ne suka mutu tun fara boren a watan Disamban 2018.

Wannan dai shi ne bore mafi muni da Shugaba al-Bashir ya fuskanta tun bayan da gwamnatinsa ta fara mulki a shekarar 1989, amma shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi ya sha alwashin ba da gudumuwar shawo kan matsalar da kasar Sudan ke fuskanta.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW