1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masu zanga-zanga sun dauki alwashin ci-gaba da zaman dirshan

Zulaiha Abubakar
May 16, 2019

Gamayyar jam'iyyun adawa a Sudan sun bayyana takaici game da dakatar da tattaunawa da masu zanga-zanga har na tsawon awanni 72 da sojoji suka yi.

Sudan Protest
Hoto: Getty Images/AFP/M. el-Shahed

Hadakar jam'iyyun mai lakabin (DFCF) ta dauki alwashin ci-gaba da zaman dirshan a harabar shalkwatar tsaron kasar ta Sudan da kuma sauran gurare. Tun da fari shugaban majalisar sojojin rikon kwaryar ya sanar da cewar dakadar da tattaunawa da masu zanga-zangar ta zamo wajibi biyo bayan karya ka'idar da bangarorin biyu suka shardantawa kansu gabanin cimma matsaya da masu zanga-zangar su ka yi.