1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da fafautukar samar da gwamnati

Ramatu Garba Baba
May 18, 2019

A gobe Lahadi bangarori masu jayayya da juna kan ragamar mulki suka amince su koma zaman tattaunawa da zummar cimma matsaya a yunkurin samar da gwamnati da ake fatan kowane bangare zai iya samun wakilici.

Sudan Khartum Proteste gegen Militär-Regierung
Hoto: AFP/M. El-Shahed

Lamarin da ke zuwa bayan sanarwar dage zaman da aka yi a sanadiyar sabanin ra'ayi. A ranar Laraba da ta gabata, majalisar mulkin soja ta wucin gadi da wakilan masu zanga-zanga, sun amince da wata yarjejeniya da ke da nufin kafa gwamnatin riko ta tsawon shekaru uku, wadda za ta kai kasar ga tsarin mulkin dimukuradiyya.

A wannan Asabar ma, akwai dubban masu zanga-zanga a harabar hedkwatar soji da ke birnin Khartoum, da ke son ganin, lallai sai sojojin sun mika mulki hannun farar hula. Watanni biyar aka kwashe ana zanga-zangar adawa da mulkin al-Bashir, da ta kai ga samun asarar daruruwan rayukan, kafin a kai ga kifar da gwamnatinsa na fiye da shekaru talatin.