1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan da Sudan ta Kudu sun fara yunkurin yin sulhu

January 28, 2012

Gwamnati a birnin Khartoum ta amince ta sako jiragen dakon man Sudan ta Kudu da ta rike.

(FILE) A file picture dated 19 January 2010 shows Sudanese President Omar el Bashir (R) and First Vice President and President of the Government of Southern Sudan, Salva Kiir Mayardit (L), participating in celebrations marking the 5th anniversary of the signing of the Comprehensive Peace Agreement (CPA) in Yambio, Sudan. Omar el Bashir has won the country's first multiparty elections in 24 years, election officials said on 26 April 2010. The polls are supposed to usher in a new era of democracy in Sudan, which is recovering from a decades-long civil war between the north and south. EPA/TIM MCKULKA - UNMIS - HANDOUT EDITORIAL USE ONLY/NO SALES +++(c) dpa - Bildfunk+++
Omar el Bashir da Salva KiirHoto: picture-alliance/dpa

Sudan a wannan asabar ta ce zata sako duk jiragen danyen man Sudan ta Kudu da ta ke rike da su domin sassauta rikicin da ke tsakaninsu ta yadda zasu cigaba da gudanar da yarjeniyoyin da ke daukan tsawon lokaci yanzu. Said Khatib mai magana a madadin wakilan Sudan ya ce wannan mataki da suka dauka ya nuna cewa a shirye suke su koma teburin tattaunawa. Jiragen ruwa uku wadanda ke dauke da kimanin garewanin mai sama da milliyan biyu suka makale a tashar ruwan Sudan, abun da kuma ya kawo tsaiko wajen gudanar da ayyukan da suka shafi tattalin arzikin Juba wanda ke dogaro kan kashi 90 cikin 100 na kudin shigowar man fetur. Ita dai Sudan ta Kudu tana zargin Sudan da sace mata danyen mai na kimanin dala milliyan dari takwas da goma sha biyar, to sai dai gwamnati a Khartoum ta ce ta karbi man ne a matsayin kudaden shigar da man da ta yi wa Sudan ta Kudun.

Mawallafiya: Pinado Abdu-Waba
Edita: Mohammad Nasiru Awal