1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan na fuskantar matsalar jin kai mafi girma a duniya

Binta Aliyu Zurmi
November 16, 2025

Mashawarci na musamman ga shugaban Amurka a nahiyar Afirka, Massad Boulos ya bayyana halin da fararen hula ke ciki a Sudan da babbar matsalar jin kai mafi girma a duniya.

Sudan Al-Dabba 2025 | Geflüchtete bereiten im Camp in Al-Dabba eine Mahlzeit zu
Hoto: AFP

Boulos ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP cewar rikicin kasar Sudan, bangaren jin kai matsala ce mafi girma a duniya a yau.

Kazalika ya bayyana cewar yana fatan nan bada jimawa ba za a cimma maslaha ta diflomasiyya a tsakanin bangarorin dake gaba da juna.

Tun bayan barkewar rikicin Sudan a watan Afrilun 2023, yakin yi yi sanadiyar salwantar rayukan dubban fararen hula tare da raba kusan miliyan 12 da muhallansu.

Da yake bayani a game da karbe iko da birnin El-Fasher da dakarun RSF suka yi, Massad Boulos ya ce,

 "A makonni biyu ko uku da suka gabata, mun ga faya-fayan bidiyon abin da ya faru, wadannan ayyukan ta'addancin sam ba za a amince da su ba. Dole ne a dauki mataki cikin sauri."

Washington ta bukaci bangarorin da ke rikici da juna a Sudan da su gagauta hawa teburin sulhu don kawo karshen wannan matsalar.

Karin Bayani: Majalisar Dinkin Duniya za ta tura tawagar bincike birnin el-Fasher na Sudan
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW