1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji sun kifar da gwamnatin al-Bashir

Abdourahamane Hassane
April 11, 2019

Bayanai sun tabbatar cewa sojoji na Sudan bayan tattaunawa da Shugaba Umar al-Bashir sun neme shi ya yi murabus da neman kama shi.

Sudan Militär und Demonstranten in Khartoum
Hoto: Getty Images/AFP

Ministan tsaro a Sudan ya yi kira na a kama Shugaba Omar al-Bashir da ma kawar da gwamnatinsa bayan watanni da aka dauka a kasar ana zanga-zangar adawa da gwamantinsa ta tsawon shekaru 30. Dubban al'ummar kasar sun kwarara a tituna don ganin yadda za ta kaya bayan da aka shiga tattaunawa tsakanin sojoji da bangaren gwamnatin ta al-Bashir.