1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Sojin Sudan sun sako fursunonin siyasa

May 30, 2022

Jaridun kasar ta Sudan sun ce kimanin mutum 125 ne hukumomi suka sako bayan umurnin da al-Burhan wanda ke rike da shugabancin kasar ya bayar a yammacin ranar Lahadi.

Sudan General Abdel Fattah al-Burhan
Hoto: Mahmoud Hjaj /AA/picture alliance

Shugaban rundunar sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan ya janye dokar-ta-baci da sojojin kasar suka sanya a lokacin juyin mulkin da aka yi a kasar a shekarar da ta gabata. Al-Burhan ya kuma umurci a sako fursunonin siyasa da ake tsare da su a kasar. 

A ranar Asabar da ta gabata MDD ta yi kira ga mahukuntan Sudan da su janye dokar-ta-bacin bayan mutuwar wasu masu zanga-zanga guda biyu a birnin Khartoum.