1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaArewacin Amurka

Sudan ta Kudu ta amince da bukatar Trump na jibge fursunoni

July 12, 2025

A daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ke kokarin aike wa da daruruwan fursunonin Venezuela zuwa wasu kasashen Afirka, an samu rarrabuwar kawuna tsakanin kasashen nahiyar.

Wasu fursunonin Venezuela da ke tsare a Tsibirin gwale-gwale na Guantánamo
Wasu fursunonin Venezuela da ke tsare a Tsibirin gwale-gwale na Guantánamo Hoto: Pedro Mattey/AFP

Kasar Sudan ta Kudu ta amince da bukatar Amurka, Ruwanda kuma ta ce tana ci gaba da tattaunawa da Trump, yayinda Najeriya ta yi fatali da bukatar Washington.

Karin bayani: Najeriya ta bijire wa muradin Trump na jibge mata bakin hauren Venezuela 

Amurka dai ta bujiro da shirin aike wa da fursunoni da bakin haure dake jibge a kasar zuwa kasashe, maimakon maida su kasashensu na asali. Amurka ta aike da daruruwan fursunonin Venezuela zuwa kasashen Costa Rica da El Salvador da kuma Panama, inda kuma take neman fadada aikinta na jigilar wadancan mutane da ta kira bata-gari zuwa Afirka da Asia da kuma Turai.

Karin bayani: Kotun kolin Amurka ta ba wa Trump damar aiwatar da munufarsa ta korar baki

Babban jami'in da ke kula da iyakokin Amurka Tom Homan ya sanarwa da manema labarai cewa gwamnatin Trump na ci gaba da tattaunawa da kasashe da dama domin waiwatar da wannan manufa ta dakile bakin haure shiga kasar ta Amurka.

Batun bakin haure na daga cikin batutuwan da shugaba Trump ya tattauna da wasu shugabannin Afirka biyar da suka gana da shi a fadar White House wadanda suka hada da na kasashen Liberiya da Senegal da Guinea-Bissau da Mauritaniya da kuma Gabon.