1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Yan RSF sun kashe mutane a asibitoci

Abdullahi Tanko Bala
October 29, 2025

Shugaban kungiyar lafiya ta duniya WHO Tedros Adhanon Gebreyesus ya ce RSF sun kashe marasa lafiya da masu jinyar su a asibitin Saudi dake el-Fasher babban birnin arewacin Darfur

Wasu 'yan gudun hijira bayan da RSF ta kwace iko da birnin el Fasher
Wasu 'yan gudun hijira bayan da RSF ta kwace iko da birnin el FasherHoto: AFP

Mayakan sa kai na RSF a Sudan sun kashe daruruwan mutane ciki har da marasa lafiya a asibitoci bayan da suka kwace iko da birnin el-Fasher da ke yammacin Darfur a cewar Majalisar Dinkin Duniya da ma'aikatan agaji wadanda suka baiyana munin ta'asar.

Shugaban kungiyar lafiya ta duniya WHO Tedros Adhanon Gebreyesus a cikin wata sanarwa ya ce marasa lafiya 460 da masu jinyar su mayakan RSF sun kashe su a asibitin Saudi da ke el-Fasher babban birnin arewacin Darfur.

Ya ce kungiyar lafiya ta duniya ta kadu matuka da lamarin.

Kungiyar likitoci ta Sudan da ke bin diddigin yakin ta ce mayakan RSF sun kashe duk wadanda suka samu a cikin asibiti har da ma'ikatan jinya da ke kula da marasa lafiyar.