Taƙaddama tsakanin Japan da China
October 16, 2012![©Kyodo/MAXPPP - 14/09/2012 ; NAHA, Japan - Photo from a Kyodo News aircraft shows the Chinese marine surveillance ship Haijian 51 (front) in Japanese territorial waters near the Japan-controlled Senkaku Islands in the East China Sea on Sept. 14, 2012. China also claims the islets and calls them the Diaoyu Islands. At back is a patrol ship of the Japan Coast Guard. (Kyodo)](https://static.dw.com/image/16309450_800.webp)
Bisa ga dukkan alamu rikicin kasashen China da Japan ya fara ɗaukar wani sabon salo, Inda yanzu kasashen biyu suka dauki matakin shiga cikin shirin ko-ta-kwana, a yayinda dakarun kasashen biyu ke cikin shirye-shiryen kasancewa a bakin daga. Wanna rikicin ya ɗauko asalinsa ne bisa wasu tsibirai da kasashen biyu ke taƙaddama akansu. Kasar China ta jibge a kalla wasu manyan jiragen yakin ruwanta takwas, a kusa ga kasar Japan yayinda kasar ta Japan ta ce tuni dakarun kasasrta ke cikin shirin ko-ta-kwana, domin maida martani ga duk wani yunkurin kasar China, na aukawa Japan. Saktarin janar na MMD Ban Ki-moon ya kira kasashen biyu da su kai zuciya nesa, domin kaucewa duk wani tashin hankali a dai-dai lokacin da duniyar ke cikin wasu riginginmu.
Mawallafi: Usman Shehu Usma
Edita: Umaru Aliyu