Shugabannin mabiya addinin Kirista a Najeriya karkashin lemar darikar LCCN sun yi kira ga 'yan Najeriya baki daya da su rungumi juna muddin ana son ci gaba me dorewa.
Talla
Bayanin hakan na kunshe ne cikin jawaban da manyan malamai na mabiya addinin na Kirista suka gabatar a yayin kammala taron darikar ta LCCN na kasa da ya gudana a jihar Adamawa da ke Arewa maso Gabashin Najeriya.