1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

tabarbarewar tsaro a Somaliya

March 21, 2007

Mutane a kalla 14 ne suka rasa rayukan su a Somalia. Hakan ya faru ne bayan wani dauki ba dadi daya wanzu, a tsakanin yan fadan sari ka noke da kuma jami´an tsaro a birnin Magadishu.

Rahotanni dai sun tabbatar da cewa wannan arangama ta baya bayan nan ta faru ne a kusa da gidan gwamnatin kasar, inda yan sari ka noken ke kwanton baunan kaiwa jami´an tsaron na kasar hare hare.

Jim kadan dai da wannan arangama, yan fadan sari ka noken suka dinga jan gawarwakin sojojin da suka halaka akan titunan birnin.

A dai watan disambar bara ne, gwamnatin kasar tare da hadin gwiwar dakarun sojin Habasha suka fatattaki yan tawayen kasar daga birnin na Magadishu.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW