1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Wasu hare-haren ta'addanci sun hallaka mutane a Burkina Faso

Abdoulaye Mamane Amadou
April 25, 2022

Rahotanni daga kasar Burkina Faso na nuni da cewa an halaka mutane 15 ciki har da sojojin kasar tara sakamakon wasu tagwayen hare-hare da 'yan ta'adda suka kai wa dakarun kasar.

Burkina Faso Gorgadji | Soldaten auf Patroullie
Hoto: LUC GNAGO/Reuters

Rundunar tsaron kasar Burkina faso ta ce an kai hare-haren a wasu sansanonin sojin kasar biyu da ke Gaskindé da Pobe Mengao a yankin arewci, kana kuma wasu fararen hula hudu da 'yan kato da gora biyu na daga cikin wadanda suka gamu da ajalinsu a cikin harin.

Sanarwar ma'aikatar tsaron ta ce an kuma samu akalla mutnane 30 da suka jikkata a jerin hare-haren na wanda 'yan ta'adda da ya auku a kusa da iyaka da Mali. Tun a shekarun 2015 ne kasar Burka Faso mai iyaka da Mali da Jamhuriyar Nijar ke fuskantar hare-haren 'yan ta'adda wanda kuma ya yi sadanadiyar mutuwar mutane da dama ciki har da fararen hula musamman a yan,kin arewacin kasar.