Rikicin Siriya ya yi sanadiyyar rayuka dubu 250
July 29, 2015![Syrien UN-Gesandt Staffan de Mistura bei Baschar al-Assad in Damaskus](https://static.dw.com/image/18054960_800.webp)
Staffan de Mistura ya fada wa Kwamitin Sulhu cewar, fatan Majalisar Dinkin Duniya shi ne, lokacin da Siriyawan za su bayyana a wurin taron, suna da kyakkyawan guzuri dangane da makomar kasarsu a siyasance, musamman yadda za a warware rikicin.
A cewarsa muhimmin abun da aka cimma a taron sulhu tsakanin manyan kasashe a watan Yunin 2012, shi ne kafa gwamnatin rikon kwarya mai cikakken iko. Hakan shi ne tubali, kafin a gudanar da zabe, wanda zai bukaci shugaba Bashar al Assad ya mika mulki a wani lokacin da ba a zartar ba.
Babban sakataren MDD Ban Ki moon, ya fada wa Kwamitin Sulhun cewar, rikicin na Siriya da ya dauki sama da shekaru yana gudana, wanda ya lashe rayukan mutane a kalla dubu 250, alamu ne na gazawar al'ummomin kasa da kasa saboda rarrabuwar kawuna da ke tsakaninsu a kan rikicin.