1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Takarar zaɓen shugaban ƙasa a Masar

March 10, 2011

Mohammed ElBaradei tsohon shugaban hukumar kula da makamashi ta Majalisar Ɗinkin Duniya ya bayyana ƙudirin sa na tsayawa takarar shugaban ƙasa a Masar

Mohammed ElbaradeiHoto: AP

Tsohon shugaban hukumar kula da makamashi ta Majalisar Ɗinkin Duniya kuma wanda ya ci lambar Nobel ta zaman lafiya, Mohammed ElBaradei ya ce zai tsaya takarar shugaban ƙasa a zaɓukan da za'a gudanar a ƙasar Masar da zarar aka mayar da tsarin mulkin ƙasar bisa turbar demokraɗiyya. A wani jawabi da ya yi a gidan Talabijin na ƙasa, Elbaradei, ya yi gargaɗin cewa har yanzu dai ba'a yi nisar a zo a gani ba, wajen gyarar fuskar da ake wa kundin tsarin mulkin ƙasar, kuma a cewar sa, abu ne da ya zama wajibi a kammala nan ba da daɗewa ba. ElBaradein dai, ya kwatanta canje-canjen, wadanda suka haɗa da ƙayyade wa'adin da ya kamata shugaban ƙasa ya riƙe madafun ikon ƙasar, a matsayin wani abun da ake gudanarwa sama sama, kuma ya yi kira ga shugabanin mulkin sojar ƙasar da su ɗage ƙuri'ar da za'a jefa dangane da sauye-sayen kundin tsarin mulkin ƙasar, wanda ake sa ran kaɗawa a ranar 19 ga wannan watan na Maris. A watan da ya gabata ne dai alummar ta Masar ta kifar da gwamnatin tsohon shugaban ƙasar Hosni Mubarak bayan da ta gudanar da zanga-zangar ƙin jinin gwamnati na wani tsawon lokaci.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu
Edita: Umar Aliyu