1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taliban ta bukaci zuwa taron majalisar Dinkin Duniya

September 22, 2021

Kungiyar Taliban ta bukaci wakiltar Afghanistan a babban taron Majalisar Dinkin Duniya na bana da kuma gabatar da jawabi a zauren majalisar.

UN Vollversammlung USA New York China Xi Jinping
Hoto: Mary Altaffer/

A cikin wasikar da ya aikawa hedikwatar majalisar, ministan harkokin waje na gwamnatin Taliban Amir Khan Muttaqi ya bukaci a bai wa kasar damar gabatar da jawabi a taron kolin karo na 76 da yake gudana a birnin New York na kasar Amirka.

A wasikar, mayakan Taliban sun bukaci yin wasu sauye-sauye na jakadun kasar, inda ta ce ta na son maye guraben wakilan Afghanistan na hambararriyar gwamnati a Majalisar da suka hada da Suhail Shaheen da kuma Ghulam Isaczai.

Tuni dai kakakin Majalisar Farhan Haq ya ce an aika da wasikar ga kwamittin da ke duba takardu, wanda shi ne ke da alhakin baiyana shugabanni da kuma wakilan kasashen da aka amince da su a Majalisar.

Tun bayan janyewar dakarun kawance na NATO da kuma Amirka, Taliban ta sami cikakken iko a Afghanistan; ta kuma sake kafa masarautar musulumci bayan shekaru 20. Sai dai har kawo yanzu ba a amince da gwamnatinta a matsayin halattaciya ba.