1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin kawo karshen yaki a Afghanistan

Lateefa Mustapha Ja'afarJuly 15, 2015

Babban jagoran kungiyar Taliban Mullah Mohammed Omar ya bayyana goyon bayansa ga batun tattaunawa da gwamnatin kasar Afghanistan.

Jagoran kungiyar Taliban Mullah Mohammed Omar
Jagoran kungiyar Taliban Mullah Mohammed OmarHoto: picture alliance/CPA Media

Mullah Omar ya amince da tattaunawar tare da wakilan kasa da kasa domin kawo karshen rikicin kasar na tsahon shekaru 13 da ya tarwatsata. A yayin da yake jawabinsa na kammala azumin watan Ramadana Mullah Omar ya ce idan aka duba a addinance ma ba a haramta tattaunawar sulhu irin wannan dama musayar bayanan sulhu tsakanin makiya ba. Mullah Omar ya kuma bukaci mayakansa da su yi iya kokarinsu wajen ganin basa kashe fararen hula a yayin gudanar da ayyukansu ya na mai cewa kare hakki da rayuwar al'umma shine ayyukansu a addinance. A makon da ya gabata dai wakilan gwamnatin ta Afghanistan da kuma na kungiyar ta Taliban sun yi ganawar gaba-da-gaba a karon farko a kasar Pakistan domin warware yakin da suka kwashe tsahon shekaru suna gwabzawa a kasar.