1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tarayyar Turai za ta kula da iyakokin Libiya

Usman ShehuMay 22, 2013

Kungiya Tarayyar Turai za ta tura wata tawaggar da za ta riga lura da kan iyakokin kasar Libiya, domin tabbatar da tsaron kasar

Libyan armed guards stand outside the coutroom during the trial of Seif al-Islam, son of Libya's late dictator Moamer Kadhafi, for illegally trying to communicate with the outside world in June last year, on May 2, 2013 in the northwestern town of Zintan. Two lawyers, one named by the court, represented him as he faced the charge of "undermining state security" for meeting four envoys from the International Criminal Court. AFP PHOTO/MAHMUD TURKIA (Photo credit should read MAHMUD TURKIA/AFP/Getty Images)
Libiyawa masu dauke da makamaiHoto: MAHMUD TURKIA/AFP/Getty Images

Shugabannin Tarayyar Turai sun amince da tura wata tawagar jama'ai fararen hula da za ta riƙa kula da kan iyakokin ƙasar Libiya. Sanarwar ta ce jami'an wadanda za su fara aiki daga watan gobe, za su tallafawa gwamnatin Libiya domin ta iya kare iyakokinta da makobtanta, ta ruwa da sama da ta ƙasa, wanda tun bayan kifar da gwamnatin kanal Gaddafi, sabbin hukumomin ba su samu iko da daukacin iyakokin ƙasar ba. Kantomar kula da harkokin ƙetare ta kungiyar EU Catherine Ashton, tace dama wannan yana cikin tsarin bayan kammala yaƙin Libiya. Shirin wanda ake saran zai laƙume kudi har euro miliyan 30, zai hada da horar da jam'an shige da fice na kasar ta Libiya da kuma sanin makamar aiki, ta yadda za su kare iyakokin ƙasar dake fadin murabba'in kilo-mita 4,300, kana a gaɓar ruwa Libiya na da iyaka mai tsawon kilo-mita 2000, inda baƙin haure ke tsallakawa zuwa Turai.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Saleh Umar Saleh