Taron ƙasashen ƙungiyar haɗin kan larabawa
June 15, 2007Yau ne ƙungiyar haɗin kann ƙasashen larabawa, ta fara zaman taro na mussamman a birnin Alƙahira na kasar Masar.
Mahimman batutuwa da ke ajendar wannan taro,sun haɗa da halin da ake ciki a Palestinu da kuma ƙasar Libanon.
Praministan Fouad Siniora na Libanon, ya gayyaci taron bayan kisssan gilar da a ka yiwa ɗan majalisar dokoki Walid Eido, ranar lataba da ta gabata.
Sannan ƙasashen larabawan za su mahaura a game da adawar ƙasar Syria, a kann batun kotun ƙasa da ƙasa da Majalisar Ɗinkin Dunia ta girka ,domin sharia´ar kisan tsofan Pamninstan Libanon Rafi Hariri.
Kazalika , taronzai duba, rikicin da ake cigaba da gwabzawa, tsakanin dakarun ƙasar Libanon, da yan takifen ƙungiyar Palestinawa ta Fath Al-Islam.
Hukumomin Libanon sun zargi Syria, da hannu a cikin wannan rikici , zargin da Damascus ta mussanta.
Masu kula al´ammura a yankin gabas ta tsakiya, sun hango cewar, taron na Alƙahira ba zai tsinana kamai ba, ta la´akari da mummuna rabuwar kanu, tsakanin ƙasashen larabawa, a game da batutuwan da tawagogin za su tantana akai.