1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Annapolis kan Gabas Ta Tsakiya

November 25, 2007
Shugabannin Isra´ila da na Falasdinawa sun isa a kasar Amirka gabanin taron kolin birnin Annapolis da za´a yi ranar talata da nufin farfaɗo da ƙoƙarin samar da zaman lafiyar yankin Gabas Ta Tsakiya. Yayin da ya yada ɗan gejeren zango a Washington shugaban Falasɗinawa Mahmud Abbas ya ce yana ganin taron wanda Amirka ta shirya a matsayin matakin farko na tattaunawar ƙarshe dangane da kafa wata ƙasar Falasdinu. Shi kuwa Firaministan Isra´ila Ehud Olmert cewa yayi yana sa rai za´a yi tattaunawa mai ma´ana.