1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron Ministocin Turai a kan Siriya

May 27, 2013

Ministocin harkokin waje na Tarayyar Turai za su yi mahawara dangane da makomar takunkumin haramta shigar da makamai Siriya da yiwuwar taimaka wa 'yan tawaye.

German Foreign Affairs minister Guido Westerwelle, Swedish Foreign Affairs minister Carl Bildt and EU commissioner for International Cooperation, Humanitarian Aid and Crisis Response Kristalina Georgieva and EU Commissioner for Enlargement and European Neighbourhood Policy Stefan Füle (LtR) talk prior to a Foreign Affairs Council on April 22, 2013 at the Kirchberg conference centre in Luxembourg. EU foreign ministers meeting are set to formally adopt measures enabling EU companies on a case-by-case basis to import Syrian crude and export oil production technology and investment cash to areas in the hands of the opposition. The Council will take stock of the reparations for the Eastern Partnership foreign ministers meeting, which will take place in July in Brussels. The Council will also look at the situation in Mali. AFP PHOTO/ GEORGES GOBET (Photo credit should read GEORGES GOBET/AFP/Getty Images)
Hoto: GEORGES GOBET/AFP/Getty Images

Cece-ku-ce dangane da yiwuwar taimaka wa 'yan tawayen Siriya da makamai, shi ne zai kasance babban ajandar taron ministocin harkokin waje na Kungiyar Tarayyar Turai da zai gudana a wannan Litinin a birnin Brussels. Wannan taron na zuwa ne a daidai lokacin da takunkumin da EU din ta kakaba wa Siriya kan shigar da makamai kasar ke karewa a ranar daya ga watan Yuni. Wannan takunkumin dai kazalika ya shafi 'yan tawayen, wanda kuma ke bukatar fadada shi idan har za a taimaka musu da makamai. Birtaniya dai ta dage ganin cewar an taimaka wa 'yan tawayen da makamai, a yayin da mafi yawan sauran kasashen Turai ke adawa da wannan yunkuri. A ganinsu dai, hakan tamkar kara ingiza rikicin kasar ne. Majiyar diplomasiyya a wurin taron na nuni da cewar, har yanzu babu masaniya dangane da ko ministocin Turan za su cimma fadada takunkumin haramta shigar da makamai Siriya ko kuma a'a. A yanzu haka dai gwamnati a Damaskus ta ce a shirye take ta halarci taron kasa da kasa da ake shirin gudanarwa domin neman mafita kan rikicin kasar. Ministan harkokin wajen kasar Walid Muallem ya tabbatar da haka a wata ziyara da ya kai birnin Bagadazan kasar Iraki.

Mawallafiya : Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Mohammad Nasiru Awal