MDD da Jamus za su jagoranci taro kan Libiya
October 5, 2020![Libyen-Ägypten-Waffenruhe](https://static.dw.com/image/53708969_800.webp)
Talla
Taron da zai gudana ta kafar bidiyo, zai samu halartar babban sakataren MDD Antonio Guterres da ministan harkokin wajen Jamus Heiko Maas, wanda ke zuwa bayan wanda ya gudana a birnin Berlin cikin wannan shekara.
Ana sa ran kasashe 16 da kungiyoyin kasa da kasa da suka halarci taron na Jamus a baya, za su kasance a taron na wannan rana ta Litinin, a kokarin da ake yi na gano bakin zaren warware rikicin kasar ta Libiya.