A babban birnin Chadi, manyan bishop-bishop na kasashe shida na yankin tsakiyar Afirka sun kammala taro karo na 13 na kungiyarsu ta ACERA, inda suka yi nazari tare da bayyana alkibla da Cocin Katolika za ta fusaknata.
Ginin CociHoto: Sodiq Adelakun/REUTERS
Talla
Yawancin mabiya cocin Katolika na Chadi sun bayyana cewar darikarsu ba ta samun angizo sosai a fagen addini a kasar idan aka kwatanta da Musulunci. Sannan sun zargi darikar da rashin kulawa da daukar matakai ko matsaya a duk da wasu munanan halaye da bangaren ikon Chadi ke nunawa.
Tasirin Cocin
Ginin CociHoto: Wirestock/Pond5 Images/IMAGO
Hasali ma dai, wadannan Kiristocin suna son ganin cocin Katolika da ke Chadi na tasiri kamar yadda cocin Katolika da ke Kwango ke yi a karkashin babban taron bishop na Kwango (CENCO), wanda a lokuta da dama ke daukar matsayi kan batutuwan da suka shafi siyasa.
Sai dai Samuel Mbaïrabé Tibibgar, Bishop na Koumra a kudancin kasar Chadi ya ce wannan sukar ba ta da tushe da makama saboda cocin Katolika da ke Chadi na taka rawar gani.
Rayuwar Paparoma Benedict XVI
Paparoma Benedict XVI na da kima a mahaifarsa taJamus. Sai dai badakalar cin zarafin yara da ake zargin limaman Coci ta dabaibaye shugabancinsa na darikar Katolika.
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler
'Mu ne PaParoma'
"Mu ne PaParoma" Taken jaridar Bild na watan Afrilu a shekarar 2005 kenan, jaridar da ake bugawa a Jamus ta dauki wannan taken ne, bayan da aka zabi Joseph Ratzinger dan shekaru 78 da haihuwa a matsayin shugaban Cocin Katolika, kafin ya koma amsa sunan Benedict XVI, ya maye gurbin Fafaroma John Paul II, ya kasance shugaban darikar Katolika na 265.
Hoto: picture-alliance/dpa/T. Kleinschmidt
Rayuwar biyayya ga Ubangiji
An haife shi a ranar 16 ga watan Afrilu a shekarar 1927, Joseph Ratzinger (daga hagu) ya yi kuruciyarsa a lokacin yakin duniya na biyu, tun wancan lokacin, ya yanke shawarar bin addinin Krista da burin zama limamin coci.
A lokacin da ake gwabza yaki, an nemi Ratzinger mai shekaru 16 da ya shiga rundunar sojin Hitler, bai jima ba kafin ya raba gari da rundunar bayan da sojojin suka dauke ido daga kanshi. An dauke shi wannan hoton a shekarar 1943. A shekarar 1944 ya shiga cikin rundunar Wehrmacht, Amirka ta tsare shi a matsayin fursunan yaki kafin ta sake shi a watan Yunin shekarar 1945.
Hoto: Getty Images/AFP/STF
Limami, Farfesa kuma Fafaroma.
Ratzinger ya karancin ilimin addinin Kirista ya kuma zama limamin coci a 1952 kafin daga bisani ya zama Farfesa a fannin ilimin addini a jami'ar Regensburg, a lokacin ya na da shekaru 30. Ana ma sa kallon mutum mai son ganin ci gaban addinin Kirista, amma bayan wata zanga-zangar da wasu dalibai suka gudanar a shekarar 1960, aka soma yi mi shi kallon mai ra'ayin 'yan mazan jiya.
Hoto: Getty Images/AFP/KNA
Ya sami goron gayyata ta musanman
A shekarar 1981, shekaru hudu da zama archbishop na biranen Munich da Freising, Fafaroma John Paul II ya gayyaci Ratzinger zuwa fadar Vatican da ke birnin Roma. Ya kuma karrama shi da mukami mai girma, daya daga cikin manyan mukamai na Cocin Katolika, matakin ya ja hankalin wadanda ke ganin ba shi da gogewa sosai a aikin limanci.
Hoto: picture-alliance/dpa
Ra'ayin rikau
Kardinal Ratzinger ya kasance mai ra'ayin rikau, ana kwatanta ra'ayinsa da na Paparoma John Paul II. Ya sha baiyana matakinsa na adawa da zubar da ciki da shan magungunan hana haihuwa, ya kuma tsaya kai da fata kan wadannan batutuwan har zuwa karshen shugabancinsa a cocin.
Hoto: picture-alliance/dpa
Rudani a Cocin Katolika
A shekarar 2009, Fafaroma Benedict XVI ya sha suka bayan da ya dage haramci daga kan wanu limaman cocin da aka samu da laifin karyata aukuwar kisan kiyashi na Holocaust, baya ga haka ya sha suka kan boye laifukan cin zarafin yara kanana da aka tafka na tsawon lokaci a yayin shugabancinsa. Wadannan batutuwan sun dabaibaye shugabancinsa.
Hoto: Getty Images
Zarge-zargen cin zarafi
Benedict ya yi kokarin shawo kan badakalar lalata da kananan yara, ya bayar da damar tattauna wa da wadanda lamarin ya shafa, ya kwatanta laifin cin zarafin yara da wata annoba mai matukar wahala ga wadanda aka ci zalinsu, duk da cewa ya tsaurara matakan horas da limamai, masu sukarsa na ganin gazawarsa, idan aka kwatanta da matakin da magajinsa ya dauka na shawo kan lamarin.
Hoto: picture-alliance/dpa
Suka daga Jamusawa
A yayin ziyararsa a Jamus a shekarar 2011, Benedict XVI ya sami tarba ta musanman daga al'ummar kasar, amma kuma ya sha suka daga wasu. Da dama sun soke shi kan gazawar da ya nuna ga wadanda limaman coci suka ci zarafinsu da kuma kin amincewa da ma'auratan da ba mabiyan darikar Katolika ba.
Hoto: picture-alliance/dpa
Fusata al'ummar Musulmi
Wani hoton barkwancin Fafaroma ne a yayin wani bikin karnival a birnin Mainz a shekarar 2007 da ke nuna yadda Benedict XVI ya kutsa kai a cikin masallaci, mai zanen na kokarin isar da sako kan furucin Fafaroman da ke cewa, Sarki Manuel II Palaiologos ''Ya zargi annabi Muhammadu da janyo wa duniya bala'i,'' kalaman sun fusata Musulmi da haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin mabiya addinin Islama.
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Dedert
Ganawar shugabanin Cocin Katolika
A yayin da ya yi ritaya a shekarar 2013, Benedict XVI ya yi alkwarin tsuke bakinsa daga al'amuran cocin kamar yadda Fafaroma John Paul II ya yi, sai dai a shekarar 2020 ya kaddamar da wani sabon littafi da ya rubuta, inda a ciki ya ce, ba zai yi shuru a dangane da dokokin da suka shafi rashin auren Fafaroma ba.
Hoto: Reuters/Vatican Media
Amincewa da gazawa
A watan Janairun 2022, Fafaroma mai murabus ya nemi afuwa kan shedar karya da ya gabatar a lokacin bincike kan laifuka na cin zarafi da aka aikata a lokacin da ya ke limami a Munich.
A takardar da ya gabatar, ya ce, an samu akasi amma ba wai ya yi hakan da wata manufa ba, sannan ya kare matakinsa da cewa, bai gurfana a gaban kuliya ba a lokacin da ake shari'ar a shekarar 1980.
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Hoppe
Hotuna 121 | 12
Irin wannan ra'ayi shi ne ma masanin kimiyyar siyasa na Chadi Evariste Ngarlem Toldé, ya yarda da shi, inda ya jaddada cewa, Cocin Katolika na gudanar da shirye-shirye da aikace-aikace da yawa a fannin zamantakewar al'umma a tsawon tarihinta.
A bisa ga kidayar jama'a ta karshe da aka gudanar, mafi yawan al'ummar Chadi Musulmi ne, inda take da kusan kashi 55% na Musulmai da kuma kashi 41% na Kiristoci. Sannan daga cikin wadannan Kiristoci, adadin mabiya darikar Furotesta ko Evangelic ya dan zarta mabiya darikar Katolika. Me yiwuwa, wadannan alkaluma ne ke bayyana raunin tasirin Cocin Katolika a Chadi.