1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tasirin kalaman Janar Babangida a siyasar Najeriya

Uwais Abubakar Idris
February 21, 2025

Fitowa fili da tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya yi na bayyana cewa marigayi Chief Abiola ne ya lashe zaben June 12 1993 da ya soke, ya haifar da muhawara tsakanin al'ummar kasar.

Janar Ibrahim Babangida ya yarda cewa Moshood Abiola ne ya lashe zaben June 1993
Janar Ibrahim Babangida ya yarda cewa Moshood Abiola ne ya lashe zaben June 1993Hoto: D. Faget/AFP/Getty Images

Bayan kwashe shekaru 32 ne tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya Janar Ibrahim Badamasi Babangida da kansa ya warware takunkumin da ya sanyawa bakinsa a kan zaben 12 ga watan yuni da ya sauya alkiblar siyasar Najeriya. Bayan amsa cewa lallai marigayi Cif Moshood Abiola ne ya lashe zabe, ya kuma dauki nauyin dukanin  abubuwan da suka faru. Dr Yunusa Tanko, dan siyasa da ke cikin wadanda suka yi gwagwarmayar soke zaben June 12 a shekarar 1993 ya ce  Janar Babangida ya tayar da fami ne a kan mumunan raunin da zaben ya yi a Najeriya. 

Karin bayani: Makomar Jam'iyyun adawa a Najeriya

Ko da yake kalaman da Janar Babangida ya yi ba sabon abu ba ne daga tunanin mafi yawan al'ummar Najeriya da suka yi imanin cewa Cif Abiola ne ya sanya fuskantar tayar da karaya baya musamman daga bangaren 'yan kabilar yarabawa. Amma Farfesa Abubakar Umar Kari, masanin kimiyyar siyasa da ke jami'ar Abuja.ya ce akwai abubuwan da za su iya sauyawa a fagen siyasar Najeriya.

Karin bayani: Siyasar sauya sheka a Tarayyar Najeriya

Moshood Abiola: wanda ya lashe zaben 12 June 1993, amma sojojin Najeriya suka sokeHoto: picture-alliance/dpa

Mafi yawan al'umma Najeriya na kallon Janar Ibrahim Badamasi Babangida a matsayin mazari da ba a san gabanka ba, amma duk da cewa shi soja ne, Dr Kabiru Danladi Lawanti na ganin cewar akwai darussa daga abin da ya faru. Soke zaben na June 12 dai ya sanya Najeriya shiga mataki na lallashi ga kabilar Yarabawa a 1999, inda aka lalubo da tsohon shugaban kasar Cif Olusegun Obasanjo a kokari na yi wa lamarun saiti. 

Karin bayani:Sharhi kan siyasar ubangida a Najeriya

A yayin da kalaman Janar Babangida suka kara fito da abubuwa a fili, zaben na June 12 zai ci gaba da kasancewa wanda ba za a manta shi ba a tarihin Najeriyar musamman a yanzu da kasar ta kara dagewa a kan mulkin dimukuradiyya.