Makomar Siriya a siyasance
December 26, 2015![Staffan de Mistura / Syrien / UN](https://static.dw.com/image/18264843_800.webp)
Talla
Jakadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan harkokin Siriya Staffan de Mistura ya bayyana fata da ke akwai na shiga tattaunawa da bangarori masu gaba da juna a kasar Siriya, wato bangaren shugaba Bashar al-Assad da bangaren 'yan adawa tun daga ranar 25 ga watan Janairu a Geneva kamar yadda ofishin jakadan ya bayyana a ranar Asabar din nan.
A cewar jawabin da ke fitowa daga ofishin na De Mistura ana kara azama kan duk wasu matakai da za su kai ga wannan tattaunawa a wannan rana da aka tsara tare da neman hadin kan dukkanin bangarorin, sannan jawabin ya kara da cewa ba za a yi sakaci ba shirin da aka fara samun ci gaba a kansa na tattaunawar sulhu ya fiskanci wata matsala.