1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump na duba yiwuwar kawo karshen yakin Iran

Binta Aliyu Zurmi
March 21, 2026

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa yana duba yiwuwar kawo karshen hare-haren sojin da suke kai wa kasar Iran nan bada jimawa ba.

USA Washington D.C. 2025 | Donald Trump unterzeichnet den "Genius Act"
Hoto: Nathan Howard/REUTERS

A wani sakon da ya wallafa a shafin sada zumunta na Truth Socials, Trump ya ce sun kusa cimma muradunsu a yakin da suke yi da Iran, don haka suna duba yiwuwar kawo karshen ayyukan sojoji a yankin Gabas ta Tsakiya kan kasar Iran.

Kazalika Trump ya ce alhakin kula da ayyukan dake gudana a mashigin ruwa na Hormuz zai koma ga kasashen dake amfana da shi.

Farashin mai a kasuwannin duniya na ci gaba da tashin gouron zabi tun bayan rufe mashigin Hormuz da kasar Iran ta yi.

A baya dai shugaban na Amurka ya yi kira ga kasashen yamma don goya masa baya na kare mashigin, kiran da kasashe irinsu Jamus da Burtaniya da Faransa suka juya wa baya, matakin da ya ce ka iya yin barazana ga kawancen NATO.

Karin Bayani: