1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump: NATO ta kara kudadenta na tsaro

July 11, 2018

Shugaban Amirka Donald Trump ya yi kiran kasashe mambobin kungiyar NATO su kara yawan kudaden da ake kashe wa harkoki na tsaro.

Belgien Nato-Gipfel
Hoto: Reuters/K. Lamarque

Shugaban Amirka Donald Trump ya yi kiran shugabannin kasashe mambobin kungiyar tsaro ta NATO da su kara yawan kudaden da ake kashe wa harkoki na tsaro.

Yayin jawabin da ya gabatar lokacin taron jagororin kungiyar a Brussels babban birnin kasar Beljiyam, Mr Trump ya ce kamata ya yi a rika samar da kashi hudu cikin 100 na kudaden da ake samu daga kayayyakin da ake sarrafawa a cikin gida, akasin kashi biyu cikin 100 da suke samarwa a yanzun.

A share guda kuwa shugabannin na NATO sun amince da wasu muhimman batutuwa, musamman irin takun-sakar da ake samu tsakanin kasashen mambobin kungiyar.

Sun kuma amince da mika gayyata a hukumance ga kasar Macedonia da ta shigo cikin kawancen, bayan sasanta ta da aka yi da makwabciyarta wato kasar Girka.