SiyasaGabas ta Tsakiya
Trump ya kosa da yaki da Iran
June 10, 2026
Talla
Shugaba Donald Trump na Amurka ya bayyana cewa Iran tana bata lokacin wajen tattaunawa kan samun zaman lafiya, kuma kasar ta Iran za ta fuskanci sakamakon abin da take aikatawa.
Lamura sun kakare
Shugaba Trump wanda ya wallafa haka a shafinsa na sada zumunta, bai yi wani karin haske ba, bisa abin da yake nufi.
Amma wannan ya zama manuniya da kosawa da ya yi kan samun yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu.
Kalaman na Shugaban Amurka suna zuwa bayan kasashen biyu sun sake yin musanyen wuta, inda Amurka ta kai hare-haren bayan wani hari kan jirginta mai saukan ungulu, ita kuma Iran ta mayar da wuta kan kasashen yankin da suke da sansanonin sojan Amurka.