Trump ya soke duk manufofin gwamnatin Joe Biden
November 29, 2025
Shugaban Amurka Donald Trump ya sha alwashin soke duk wasu manufofin tsohuwar gwamnatin jam'iyyar Democrat karkashin Joe Biden, yana zargin Biden ya yi amfani da sa hannu kan wasu manufofi da 'autopen' naurar kwaikwayon sa hannu kan wasu tsare-tsaren gwamnati.
A cikin wani sako da ya wallafa Intanet, Trump ya sanar da soke kashi 92 cikin 100 na umrnin da Joe ya amince da su a gwamnatinsa ciki har da batun baki da yarjejeniyar muhalli da kuma dai-daito da batun ma'aikata.
Wannan dai na zuwa ne yayin da Trump ya dakatar da duk wani yunkuri na masu neman mafaka a Amurka, bayan da wani dan kasar Afganistan ya kashe wata jami'ar tsaron kasar guda daya tare da raunata wani a babban birnin kasar. Matakin ya sa hukumomin Amurka fara nazari kan masu katin zama na wucin gadi 'green cads' da aka baiwa wasu mutane daga kasashe 19.
Gwamnati ta kuma dakatar da duk wasu shirye-shirye na tsugunar da 'yan kasar Afganistan a kasar tare da fara nazarin wadanda aka ba wa izinin zama a karkashin gwamnatin Biden da ta gabata.
Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta kuma dakatar da bayar da biza ga mutanen da ke rike da fasfo din Afghanistan, in ji sakataren harkokin wajen kasar Marco Rubio.