1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Trump ya zargi Iran da karya yarjejeniyar tsagaita wuta

April 21, 2026

Shugaban Trump, ya zargi Iran da karya yarjejeniyar tsagaita wuta sau da dama a kan rikicin Gabas ta Tsakiya, yayin da kasashen biyu ke tattaunawa kan yiwuwar sake fara sabon zagayen tattaunawar zaman lafiya

Shugaban Amurka Donald Trump
Shugaban Amurka Donald TrumpHoto: Brendan Smialowski/AFP

Trump ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a dandalinsa na Truth Social, inda ya ce Iran din ta karya wannan yarjejeniyar ba ma sau daya ba, yana mai nuni da yarjejeniyar makonni biyu da ake sa ran za ta kare zuwa ranar 22 ga wwatan Afrilu, bayan haka yankin na iya komawa wani sabon babi na rikici mai zafi.