SiyasaJamus
Jamus za ta sake tsawaita bincike kan iyakokinta
August 7, 2025
Talla
Ministan cikin gida na Jamus Alexander Dobrint; ya ce yin hakan wani mataki na yaki da bakin haure, lamarin da ya haifar da cece-kuce tsakanin kasashen da ke makwabtaka da kasar.
Jamus ta sake kafa bincike na wucin gadi a dukkanin iyakokinta a ranar 16 ga watan Satumba, na shekara ta 2024, na tsawon watanni shida a zamanin mulkin Olaf Scholz, kafin sabon firaminista Friedrich Merz ya karfafa binciken kan iyakokin:
Bisa alkalumman da ma'aikatar harkokin cikin gida ta Jamus ta fitar, an mayar da jimillar mutane sama da dubu tara a kan iyakokinta tsakanin takwas ga watan Mayu zuwa 31 ga watan Yuli na wannan shekara.